Hukumar NAHCON ta kirkiro Manhajar da za ta rage batan alhazai lokacin Hajji

Hajji Yana daya daga cikin Shika-shikan Musulunci guda biyar, dole ne ga kowane musulmi/ma ya je hajji idan yana da hali


Hukumar da ke kula da Mahajjata Yan Najeriya ta ce ta fito da manhajar da za ta takaita batan alhazanta a lokacin Aikin Hajji. Kumar ta na cewa manhajar ta G. P. S za ta dinga jagoranci wajen nuna ma Mahajjatanta taswirar inda suke da kuma inda suke nema.
Manhajar da zasu yi amfani da ita tana dauke da yanar gizo (intanet) kuma an sanya ta a dukkan shemomin jihohin kasar, ta yadda za a iya latsa duk wacce mutum ke nema daga ko ina, kamar filin Arfa da Muzdalifa da wajen jifa.
A nan take Manhajar za ta nuna wa mutum taswirar inda zai bi ta manhajar Goggle Map.
Kamar yadda BBC Hausa ta ruwaito Manhajar za ta yi aiki ne kawai a wayoyin tafida gidanka. Haka kuma Hukumar ta NAHCON ta ce ta samar da wasu lambobin waya da alhazain Najeriya za su iya kira dare ko rana domin neman taimako. Shugaban hukumar ta NAHCON Abdullahi Mulhtar ya yi kira ga duk Alhajin da ya kira lambar ba a saurare shi ba, da ya kai korafi a shirye suke su dauki mataki.
A kowace shekara daruruwan alhazai ne ke bata, inda suke shan bakar wahala tsakanin shemomi yayin neman tantinansu.

0 comments:

Post a Comment

Thank You for Your Comment