HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 8



HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 8

 


*** *** ***
Kwanci tashi ba wuya a wurin Ubangiji, saura wata biyu cif! Auren farida, bangaren Mukhtar kuwa saura kwana biyu lokacin da aka diba masa ya cika. Wannan karon ya shiga damuwa matuka, hatta Mom hankalin ta ya tashi ganin yadda Mukhtar ke neman fita hayyacin sa, ka ganshi ya rame, ya dishe. Abin da ke daure ma iyayen kai kenan, sun rasa dalilin wannan tashin hankalin da yak e shiga.
Farida kuwa text din da take samu yanzu ya daina tada mata hankali, sai dai abin da ta kasa fahimta canjin yanayin da take samu duk lokacin da wannan text ya shigo wayar ta.
Mukhtar yana cikin falo, ya kasa fita yau ko zuwa office, kan shi ke masa tsananin ciwo, ya sha magani amma duk a banza. Shi ma kan shi ya san tsananin damuwa ce,ta haifar mishi wannan. A hankali ya lushe idanun shi ya shiga tunani kala- kala, sai dai kuma ciwon kan sai karuwa yake balle zuciyar shi ta samu nutsuwar da zatayi tunani.
Farida ta shigo ta same shi a haka, nan da nan hankalin ta ya tashi ta tsani taga yayan ta cikin damuwa cikin kidima take tambayar shi “yaya lafiya? Don Allah Yaya ka...” bata ida maganar ba sai kuma hawaye, ya shiga lallashin ta hadi da share mata hawayen da suka zubo mata, ya dan kalleta hadi da saukar da ajiyar zuciya “farida ki daina saurin hawayen nan kin ji ko? Ba na son kina zub da hawayen nan naki nakan kara shiga wata damuwar kin ji?.  Daga kai ta yi alamar eh. Ya dan saukar da ajiyar zuciya yana kallon ta, ya kauda kallon da ya ke mata hadi da komawa cikin kujerar, zuciyar shi na tattare da damuwa, wanda sam baya son kanwar shi ta fahimta.
Farida ta gyara zaman ta hadi da cewa, “wai don Allah yaya wace irin damuwa kake son sa ma zuciyar ka?” ya dan yi gajeren murmushi duk da kan shi da ke mishi ciwo, “farida tunani da kuma damuwa a yanzu sun zama mini dole, musamman da yake saura kwana biyu lokacin da Dad suka diba mini ya cika, na so in yi karfin hali in sanya ma zuciya ta hakuri na kasa hakura, gaskiya bazan iya wannan auren da za su hada ba, nika dai nasan yadda zuciya ta ke ji. Ta danyi shiru sai dai tana zargin yayan na ta anya kuwa ba wata wadda yake so? To kuma idan haka ne me zai hana ya fito fili ya bayyana tunda ba hana shi auren wacce yake son za’a yi ba, yafi wannan hadin auren da za’a yi masa alhali baya so, dan dama Sadiyar na matukar kaunar shi.
Ta ci gaba da maganar da take yi “yaya gaskiya alamomin ka sun nuna akwai wacce ka ke so, sai dai kuma ka kasa furta hakan ga ko wace ce,. Gani na ke ba wata ‘ya mace, da zaka nuna ka na so ta ki amince   maka, sai dai wani ikon Allah na daban. Yaya duk wannan tunanin da kake yawan tafka ma zuciyar ka ba abin da zai kara maka face   tsananin damuwa. Ka fito fili idan gaskiya da wacce  kake so ka fada, ba ka fada ba ya za’a yi iyaye su sani balle ita yarinyar, idan ma da abin da kake shakka duk wannan yanzu kauda shi zaka yi ka ceci zuciyar ka.
Duk maganganun da take ya kasa cewa kala, sai wani kallon ta yake, sai dai kuma a zuciyar shi yana jaddada maganganun ta, gaskiya ta fada, ya rasa yadda zaiyi da kanshi har yanzu ba a bin da zai yi face   neman zabi wurin Allah. Ya san wannan karon idan ya saba ba karamar rigima za’a saka mishi ba, koda yake ba wata rigima tunda har sun zarce   hukun cin hada shi aure da Sadiya. A nan kuma yadan yi gajeren murmushi wanda yake tattare da damuwa, har yanzu a zuciyar shi yake maga shi dai da sun zaba ma yarinyar nan wani mijin tun da bashi kadai Allah ya halitta ba, shifa bazai yadda da wannan hadin auren ba, tun da yana da wacce, yake so, acewar shi ai yanzu an daina wannan, kuma ma tunda shi ba karamin yaro bane ai ya kamata abarshi ya zaba ma kan shi. wata zuciyar ke ce mishi to ai ba ana nufin tilas ta maka ba ne, zabi biyu ne wanda ya zama dole ka zabi daya, idan baka yadda da auren sadiyar ba kayi tunanin wacce,   zaka aura” al’amarin ya masa zafi da yawa, shi dai auren nason zo mishi da matsaloli barkatai.
Duk abinnan kanwar ta shi na kallon shi, ita yanzu al’amarin shi mamaki yake bata, ganin take wannan lamarin mai sauki ne, amma shi ya dauke shi wata babbar matsala, koda yake ba tada tabbacin abin da ke damun shi, bata son yi mishi shishshigi cikin al’amurra balle ta matsa masa da tambaya, sai dai ta yi alkawari ko menene zata taya shi addu’a. mikewa ta yi ta nufi bangaren ta saboda ta tsani taga yayan hata cikin  yana yi na damuwa, tana da zurfin ciki sai dai aganin ta yayan ta yafi ta zurfin ciki duk yadda akayi akwai matsala tare da wannan al’amari na shi. ta bar yaya mukhtar wurin, wanda ya bita da kallo.
Ta na isa bangaren nata gaba daya daki ta shiga haka kawai ita ma bata jin dadin jikin ta, kwanci ta yi saman gado hadi da dan rufe idanu kamar bacci ta ke, a hankali take jin faduwar gaba, sai dada karuwa take Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un ta rika ambato  ta dan samu sauki, ta shiga tunani dai dai lokacin Usman ya kira ta, ta zura hannu ta dauki wayar hadi da karawa g a kunne, hirarsu suke cikin natsuwa ta ma’abota soyayya tana jin dadin hirar ta shi ba ta gajiya da sauraren muryar shi.
Cikin hirar Usman ke Cewa, “Farida ki na jin yadda na ke ji kuwa?” tadan yi murmushi “kamar ya kenan” ita ma ta tambaye shi , “Farida koda yaushe son ki dada karuwa yake a zuciya ta, ji na ke kamar in matso lokacin auren nan na mu, ni gani na ke watan nan biyu sun yimin nisa. Farida ina son ki bazan iya jure rashin ki ba kiyi min alkawari ki so ni tamkar yadda nake son ki. Tadan yi murmushi, bai jira tace  wani abu ba, sanyayyun kalaman shi ya rika gaya mata, su na ratsa zuciyar ta, ta lunshe idanun ta, ita kadai ta san yadda take jin dadin kalaman, ta yi tabbacin Usman ya riga ya zama wani gurbin zuciyar ta. A karshe suka yi sallama, kwantawa ta sake yi ta rufe idanun ta kamar me bacci, sai dai ta na tunano kalaman Usman, ya riga ya yi kyakkyawan zama a zuciyar ta.

*** *** ***

0 comments:

Post a Comment

Thank You for Your Comment