HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 14



HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 14




Farida kam tana tattare da RASH IN SANIN takamaiman inda maganar ta dosa, duk da haka ta razana, ta kidime,ta rude, harma da gigicewa. Jikin ta wani makarkata yake, kada dai ace   ba iyayen ta bane?. Ita kam taga tashin hankali, wani kuka ta saki mai tsuma zuciya, Dad din ya kasa koda motsi wurin da yake balle bakin shi ya iya furta wani abu. Shikam mukhtar hankalin shi ya kara tashi dama yasan hakan zata faru to amma yaso su fahimce shi bayin shi bane shikam haka Allah ya halitta mishi son ta tun tana karamar ta ya dai kasa furta hakan ne gudun irin wannan.
Tunanin farida ya katse lokacin da inna ke cewa, “dama nasan a kwana a tashi hakan zata faru, abin da nake wa gudu kenan, kada azo yarinyar nan ta girma wani cikin zuri’a ta ya kinkima, haba! Mukhtar da hankalin ka, da wayon ka Duk ina kaifin basirar da Allah ya ba ka? Shin ma ina tunanin ka? Ka rasa wacce  zaka ce   kana so duk fadin duniyan nan sai  shegiya. Mukhtar ya runtse idanun shi baya son kalaman nan da inna ke furtawa, “inna ki daina ce  mata shegiya alhali ba shigiya  bace,  , kin san hakan ba kyau” innar wata harara ta yi masa “ai sai ka nuna min iya yenta; yarinyar da aka tsinta zakace  ba shegiya  bace, to gaya min mecece? Yanzu ba wata matsala” inna ta dudi Dad din dake zaune ya rasa abin cewa bai so wannan katobarar da Mukhtar ya yi ba ya na tausayama yarinyar, innar ke cewa “Wallahi Ibrahim duk tausayin da zakaji na yarinyar nan sai ta bar gidan nan yanzunnan bawani abin da zakacemin. Ba yauba na sha gaya maka nifa irin wannan nakewa gudu to yau ga Magana ta.

0 comments:

Post a Comment

Thank You for Your Comment