HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 10



HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 10



*** *** ***
Usman ya dawo gida, bayan ya fito daga office, ba wani jimawa ba duka duka idan ya yi minti arba’in da dawo wa, Baban nashi ya kira shi.
Ya nufi kiran da ake mishi, ya sami iyayen na shi, cikin nuna alamar biyayya ya sami wuri ya zauna.
Alh umar ya dan yi gyaran murya ya fara yi mi shi Magana, da farko nasiha ya rika yi mishi, usman kam ya rasa inda maganganun suka dosa. Alh ya ci gaba “Usman ka yadda da yin Allah komai na duniya yakan tsara shi ta yadda ya so ko ba haka ba? Usman ya ce, “haka ne Baba” “yawwa” Alh yace, da shi sannan ya ci gaba “Usman karnar yadda nasan ka tun farko kai da ne mai biyayya da kuma bin umurnin, na gaba da kai wanda nake fata ka dore da hakan har illa ma sha Allah.
Usman ba wani abu ba ne face   auren nan na ka, gaskiya yanzu zan so ka janye maganar auren nan na ka, na san yarinyar da kake nema yarinya ce,  mai mutun ci, da kamun kai. Wanda hakan aka samu banban ci a wurin mahaifin ta, bai dauki mutum da daraja ba, kai ma kan ka zaka so a ce sirikin ka na tattare da dabi’u na gari. Mutane da dama sun san ya’yan Alh Ibrahim, suna da halayyar kirki, wasu har mamaki suke yi basu yo halin mahaifin su ba ko kadan.
Gaskiya nayi nadamar barin ka har maganar auren nan tayi nisa, yarinyar ta cancanta, sai dai gaskiya halayyar mahaifinta bata yimin ba ko kadan, Usman ka nemi aure gidan mutun ci wayan da kuma suka san darajar dan Adam zai fi mutun ci, ni kai na zan samu kwanciyar hankali. Saboda haka maganar aure kai da Farida babu ita daga yau. Kan haka naga ya dace in hada ka da diyar aminina Alh Abubakar, kuma har nagama Magana da shi, kai ma kanka ka sani mutum ne mai daraja ga jama’a , ya’yan sa shima gwargwado sun sami tarbiya ta gari. Saboda haka na riga na zaba maka mata da yau, dama hakkin iyaye ne auren fari su zaba ya’yan su, imba yanzu da zamani ya canzaba.
Duk maganar da Alhajin keyi ba wadda Usman yaji, tun lokacin da kunnen sa yaji Alh nacewa, “zan so ka janye maganar auren nan naka....” Wani zazzare ido ya yi saboda ya ji maganar a bazata, bai taba tunanin Alh zai masa haka a ran shi ba, sai gashi rana daya al’amarin ya zo mishi. Numfashinsa har wani kokarin daukewa yake, zuciyar shi na kokarin bugawa, saboda lokaci guda ta shiga yi mishi matsanan cin ciwo. Shi ma kanshi Alhajin hankalin shi ya ta shi, hakika ya tausayamishi sai dai kuma maganar gaskiya ya riga ya fada ba zai canza ra’ayi ba.
Shi kam Usman ya riga ya san ba zai iya rabuwa da Farida ba, shi ka dai yasan irin son da yake mata, yana matukar kaunar ta, tariga ta zamo mai wani gibi na zuciyar sa, bai yi zaton duk fadin duniyannan akwai wata macen da zai so tamkar ta ba. Sai dai kuma a tunanin shi kila mutuwar shi ta zo shi yasa ake kokarin raba shi da Farida. Da kyar ya iya tashi da zaunen da yake ba tare da y ace wani abu ba ya nufi bangaren shi. Kwantawa ya yi yana tunano soyayayar shi da Farida, soyayya ce   mai tsafta da natsuwa, lokaci guda wani tsananin son ta ya kara dira a zuciyar shi. Zumbur ya mike zaune kamar wani tababbe, ya rike kai saboda tsananin ciwon da yake mishi, ya fara gani dishi- dishi saboda jiri- jiri da yake gani, ya koma ya kwanta ko zai samu sauki, amma ina! Har yanzu zuciyar shi zafi take mishi, ya rasa inda zai saka kanshi.
Wasu zafaffun hawaye suka tararo mishi, wai me yasa za’a yi mishi haka? Shifa gaskiya ba zai fasa wannan auren ba, zaiyi iya kokarin sa don ganin ya shawo kan mahaifin sa, ji yake da a raba shi da farida gwanda ma ace, ya rasa ranshi gani yake hakan zaifi masa sauki, lokaci guda kuma zazzabi ya zo ya rufe shi.
Farida kam faduwar gaba take yawanyi ba abinda ta ke sai yawan ambaton Inna lillahi wa inna i sai kuma ta rika jin bata jin dadin jikin ta. Dare ya yi ta kasa bacci haka kawai, ita kan ta abin ya bata mamaki, ganin ta kasa baccin, dauro alwalla ta yi ta zo ta yi nafila, sannan ta bude kur’ani ta ci gaba da karantawa, a hankali ta ji ta fara samun natsuwa, ta yi addu’o’in ta ta shafa ta koma ta kwanta. A hankali bacci ya dauke ta.
Yaya Mukhtar kuwa sam kasa baccin ya yi, shima yana tunanin tashi matsalar, da yaga tunanin ba in da zai kaishi, shima alwalla ya yo ya ci gaba da sallar nafila yana rokon Ubangiji cikin kaskantar da kai har kusan subahin.
Washe gari Usman ya sami mahaifin shi, AIh Umar tausayin dan na shi ya kama shi sai dai kuma maganar shi kaifi daya ce  ba canji, har yanzu yana nadamar barin Usman da ya yi nisa wurin neman auren, bai san dalilin da ya hanashi ya hana dan tun farko ba shima yana zargin kanshi da yin kuskure. Usman ya kaskantar da murya yana ba mahaifin shi hakuri cewa, kada ya raba shi da farida kuka ya saka mishi tamkar karamin yaro, amma duk  a banza, nan danan Alh. Ya shiga yi mishi fada ce wa ya na son mai da shi mutumin banza.
Dole Usman ya fito, daki ya shiga ya kulle kansa, hawaye ke ci gaba da zubo mishi, ya lalubo wayar shi ya kira Farida, jin muryar ta ke kokarin mantar da shi halin da yake ciki, ya jima yan a Magana da ita. A je wayar keda wuya tunani ya dawo masa sabo fil! Ya rasa hanyar da zaibi ya shawo kan wannan matsalar, nan danan zuciyar shi ta rika yi mishi wani zafi, mirgina ya rika yi kan gadon hadi da hawaye, sai kuma ya mike ya rika safa da marwa cikin dakin.
Bangaren farida kuma bayan ta aje wayar, haka kawai ta shiga zurfaffen tunani wanda ba ta iya cewa ga dalihin yin shi ji take yau ta tashi da bacin rai, ba ta jin dadin zuciyar ta, kamar ta saka kuka. Yawaita addu’o’i ta rika yi, ta na neman sassauci da kuma tsari a wurin Ubangiji. Tunanin ta ya katse lokacin da text ya shigo wayar ta, har yanzu ba number kamar haka:
 Farida ki tallafi rayuwa ta kada ki juya mini baya a lokacin da ki ka San ainihin ko ni waye.

0 comments:

Post a Comment

Thank You for Your Comment