HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 4

HAUSA NOVEL BOOKS: RASHIN SANI…1 BY SARATU M. SANI SERIES 4

 *** *** ***


An kammala komai na auren farida da kuma Usman, hadi da sanya ranar aure nan da wata biyar, anyi hakan ne ko yaya mukhtar zai fidda wacce,   ya ke so a hada auren, wanda anashi bangare sam zuciyar shi ta kasa nuna mishi wacce zai zaba balle ya sa ran auren.
Zaune take cikin falo ta na kallo Yaya Mukhtar ya shigo shi ma ya zauna, sai dai s hi ba kallon ya ke ba ya dai tsura mata ido, a hankah ya lunshe idanun shi ya kwanta cikin kujerar, ta dube shi “yaya Iafiya?” “me ki ka gani” ya tambaye ta “naga kamar baka da Iafiya” murmushi ya yi “lafiya ta lau, farida kewar rabuwa dake ta fara kama ni.” Tausayin yayan na ta ne ya kama ta “haba! Yaya ka daina damuwa mana, ko yanzu da sauran lokaci kuma cekake zanbar gari.” Bai yi Magana ba sai ma kara lunsashe idanun da ya yi, ta sake kallon shi ta rasa me ke damun yayan na ta, ta dan tausasa murya “Yaya” ta kira shi “na’am yar kanwa ta ina sauraren ki” sai dai kuma ya tashi zaune saboda alamar kiran yasan Magana za ta yi da shi, ta dan saukar da numfashi a hankali ta ci gaba “yaya don Allah me ya sa ka ke baya- baya da maganar su Dad ne? ka daure yaya ka sanya musu farin ciki ka fitar da mata kayi auren nan ko hankalin su zai kwanta, duk wadda aka ce,  za’a Hada ka nan take za ka ce,  a’a sam! Kai baka tashi ba. Yaya iyayen mu basu son takura mana to me yasa kake son abun da kasan zai dame su? Yaya me yasa kake yin haka?, yaya mukhtar ya dan yi murmushi hadi da cewa”in ban da abin ki farida ba sai mutum ya samu wacce, yake so zai yi auren ba? ta dan yi murmushi ta san yayan na ta cikakken mutum ne, mai kamala da kuma kwarjini, mutum ne wanda ko wace  mace,,   za ta yi guri, ta san yadda ‘yan mata ke kururuwa a kan shi, wa su har kawan ce, su ke kullawa da ita a kan shi. Ko wace daga cikin su ba makusa a gare ta, amma abin takaici ko gaisuwa ba zai yadda ya yi da su ba, hotuna kam ya sha aiken su. Ta kauda wannan tunani ta ce,  to yaya ka bani dama in zaba maka yarinya  son kowa kin wanda ya rasa, insha’Allahu za ka yaba da zabi na.” wani dan lallausan murmushi ya yi “Farida na yadda da magar ki, sai dai kuma ni kaina nasan bayi na bane yin Allah ne. Nafison mata mai kama dake matuka, halayyar ki da sauran dabi’un ki. Farida ina son dabi’un ki sai inga ba ko wace mace ake samu haka ba, abin da yafi kawai ki bar wannan zance   ki tayani du’ai”.
Kanshi ya dauki zafi ya koma cikin kujerar ya kwanta, idanun sa sun sauya zuwa ja baya so ana tada masa zancen  aurennan an rasa dalilin wannan al’amanin nashi. Mom din tun tana kiran sa tana yi masa Magana har ta dangana ta koma yi mishi du’ai.
*** *** ***

0 comments:

Post a Comment

Thank You for Your Comment