RASHIN SANI…1
BY SARATU M. SANI SERIES 2
*** *** ***
Ta shiga gida ta nufi bangaren mom dinta, ta gaida ita mom din ta
dan yi murmushi harkin dawo? Ta ce, “eh” sai dai hajiyar ta ce, ingaya miki
idan an sake dauko wasu kayan wannan satin tana bukatar gold mai kyau, koda
yake zata kiraki ta waya ta kara yi miki bayani. Dama aiken ta mom din ta yi,
tashi ta yi ta nufi bangaren ta. Yaya Mukhtar ne ya dawo, daga office, ya gaida mom din ta su, ya dan kalli mom din
ya ce, “ina Farida ne”? tana sashen ta ita
ma yanzun nan ta dawo da aiken da nayi mata, bai sake magana ba ya nufi nashi
bangaren.
Da shigar ta bangaren nata
ta sami abincinta, nan tadan taba ci, sannan ta shiga wanka ta fito, ba tayi
wata doguwar kwalliya ba ta dauko atamfa
ta saka, atamfar ta yi mata kyau matuka dinkin yayi cif! cif! Da ita, ta fito falo, yayan na ta ne ya fito ya same
ta; ta dan fadada murmushin ta ta gaida shi ya sami wuri ya zauna kusa gare ta.
Hirar su suke cikin nishadi a lokacin wayar ta ke nuna ma ta alamar kira, Usman
din ta ne tana matukar son shi a ra ta, kamar yadda shima yak e kaunar ta. Ta
dauki wayar suka gaisa daga baya suka ci gaba da hirar su, akarshe yake shaida
ma ta gashinan zuwa gidan na su. Sam ta manta da yayan ta dake wurin, tashi ya
yi ya haye sama ya barta ita kadai. Bada wani jimawa ba sai ga Usman din ya zo,
lemu iri – iri ta aje masa da sauran kayakin mutsa baki. Hirar su suke cikin
nutsuwa tare da jaddada ma juna irin kaunar da suke wa juna, akar she ya yi sallama
da ita hadi da mika ma ta manyan ledodi guda biyu kayakin cosmetics ne a ciki
ta yi godiya.
Bayan fitar Usman din ne ta
sami yayan na ta cikin falon, ta dan dube shi sai dai ga alama fuskarshi ba walwala kamar dazu, ta dan zauna kusa dashi
cikin nuna alamar damuwa ta ce, “yaya lafiya na ganka haka?” ya dan yi murmushi
“ba komai Farida kinsan akwai yanayi na rayuwa” to amma….. “ text ne ya shigo wayar
ta shi ya katse ma ta maganar ta karanta text din dauke yake da kalaman soyayya
ma su ratsa jiki ta duba da kyau ba number anyi hiding. Ta danyi gajeren
murmushi lokacin da zuciyar ta ke tabbatar ma ta Usman din ta ne, ya na dai son
tsokanarta. Text din ya shiga zuciyar ta sosai ta ji dadin kalaman, tayi saurin
kawar da wannan ta ci gaba da Magana da yayan na ta.
Da dare misalin 8:45pm text
ya sake shigowa wayar ta ta duba har yanzu ba number sai dai text din kamar
yafi na dazu, ta danyi jim ta na nazari ita dai ta san ba tada wani saurayin da
zai rika turo ma ta text dauke da sanyayyun kalamai fa ce, Usman, to idan kuwa shine meyasa yanzu zai
rika hiding number alhali bai saba yin haka ba? Ta kauda wannan tunani ta nufi
bath room wanka tayi ta fito, mai kadan ta shafa ma jikin ta, ta dan feshe
jikin ta da turare, sannan ta dauko rigar baccin ta itama ta kara feshe ta da
turare sannan ta sa, bakin gado ta zauna ta karanto addu’o’in da ta saba
karanta wa idan zata shiga bacci, tabi lafiyar gadon ta t a kwanta hadi da rufe
jikin ta kadan da tattausan bargo. Uhm ‘yar gidan Daddy kenan.
Da safe bayan ta tashi ta yi
sallah ta koma baccin ta, sai kusan
karfe tara ta tashi ta yi wanka, ta fito ta zauna bakin madubi ba wani dogon
make-up ta yi ba, powder ta dan shafa a fuskarta, sai man lebe data shafa, iya
kacin kwalliyar kenan bata cika shafa kwalli ba sam bai dame ta ba, ko bata
shafa ba ba zaka gane ba da yake girar idanun ta nada tsawo da kuma baki sosai.
Sam ra’ayin ta ba ta cika fuskar ta da
kwalliya amma duk da haka zaka ga ta fito fes da ita, duk inda ta gifta ya zama
dole a dubeta saboda jan hankali da ke gareta.
Doguwar riga tasa sai dai
kan na ta ba dan kwali hakan ya bada damar kan nata da ya sha gyara ya zuba gadson
baya, ta duba agogo goma da minti ashirin da sauri ta fito a hankali ta isa
wani makeken falo, tanan ta nufi bangaren Mom din ta, ta gaida itacikin
girmamawa da yake Dad din nasu baya gari ya yi tafiya. Ta sake bin wata hanya
zuwa wurin da suke break fast ita da Yayan na ta tasan yanzu haka yana zaman
jiran ta, tana isa shima yana isowa wurin, ya dan ja daya daga cikin kujerun
dake zagaye da dinning table ya zauna fuskar sa dauke da murmushi ta gaida
Yayan sannan ta zauna zaman ta keda wuya kamar jira ake text ya shigo wayar ta
har yanzu ba number kalaman sun fara daga mata hankali fuskar ta tanuna alamar
damuwa. Yanzu kam abun ya fara bata mamaki zuciyar ta a yanzu ta riga ta bata tabbacin ba
usman bane, to waye? Amsar da tayi kokari ta lalubo sai dai ba hali domin
zuciyar ta ta kasa fahimtar da ita komai. Haka suka kammala break din zuciyarta
cike da damuwa; Yaya Mukhtar ya fahirnci damuwar da ta samu lokaci daya, yasan
bazata yi saurin gayama mutum damuwar ta ba saboda tsananin zurfin ciki.
Bayan sun kamala Yaya
Mukhtar ya ce, “jeki dauko mayafinki mu
je gaida Inna” kakar su Haj balki kenan ta ce, “to” ba musu sai dai ita sam
bata cika son shiga gidan Inna din ba, koma ta shiga ba wani kallon arziki
innar zata yi ma ta ba balle ta kula ta, sam jininsu bai hadu ba ita ta rasa
dalilin wannan tsanar da inna ke ma ta.
Ta
dora mayafinta ga kai suka fito gida su ka shiga gidan Inna, sunyi sallama tun
kamin su shiga falon yaya mukhtar ya fara tsokanar ta wasan jika da kaka, cikin
fara’a ta amsa sallamar ganin farida yasa tadan sauya fuska sama-sama ta karba gaisauwar
da farida ke ma ta, ganin haka yasa ta mike tsaye hadi da Cewa “Inna sai
anjima” ta fito zuciyarta zafi take mata, ba tada halin ta shiga gaida ta ita
kadai tatas inna zatayi ma ta. Za kaga
ta fara maganganu daban daban, ita dai farida ta rasa me ta yi ma innar har ta
tsane ta. Shima Mukhtar ganin farida ta fita bai tsaya yima innar sai anjima
ba, balle yar hira ya fito abin sa tana kiran sa yaki tsayawa sauri yake ya
cimma kanwar tashi, nan ya barta ta shiga fada. Gida ya same ta wurin mom din su
hira take yi da ita cikin nutsuwa, ya sami wuri ya zauna ya katse hirar da Cewa,
“don Allah mom me yasa inna koda yaushe take kokarin cusa ma mutum damuwa a zuciya?”
Mom din tasan inda maganar ta shi ta nufa, ta tabbata farida inna ta taba shi
yasa yake wannan tambayar, ta dubi farida “hala kin je gaida ita ne? “eh tare
da yaya mukaje” farida ta ce da ita, mom
din ta yi murmushi “kiyi hakuri farida Sai dai ki rage yawan shiga wurin ta kin
ji ko?” ta dan yi murmushi ba komai mom nasan haduwarjine ne da kuma tsufa.”
*** *** ***
0 comments:
Post a Comment
Thank You for Your Comment