RASHIN SANI…1
BY SARATU M. SANI SERIES 3
*** *** ***
Soyayya mai karfi ta kara kulluwa tsakanin farida da
Usman, yauma kamar kullum ya zo wurin ta hira suke cikin nishadi da natsuwa,
Usman yadan tsar eta da ido ya na kallon ta, murmushi ta yi hadi da sadda kanta,
ya dan yi murmushi shidai dabi’un ta na bashi sha’awa ya katse shirun da Cewa,
“Farida” cikin sigar muryar sa mai jan
hankali da dadin saurare, ba ta gajiya da sauraren muryar shi, ta dan dago ta
kalle shi kallon na daban ne, hakan ke sa zuciyar shi na kara kamuwa da shaukin
kaunar ta. Ya ci gaba, “don Allah da gaske ki na so na?” tambayar ta ji ta ba
zata, batasan amsar da za ta ba shi ba, ta na da tabbacin ya san ta na son shi
kamar yadda ya ke son ta, sai dai batasan inda wannan tambayar ta dosa ba. Ta
dan yi murmushi “Usman to meye kuma na wannan tambayar alhali ka na da tabbaci
ina son ka?” ya dan yi sanyayyar ajiyar zuciya hadi da Cewa, “Farida ni kadai
na san irin kaunar da zuciya ta ke miki, na tabbata bazan iya cigaba da rayuwa
ba tare da ke ba, na kan zama kamar marayen da ya rasa Uwa idan ba ki kusa
dani, farida tsananin son ki kan sa ni kuka hadi da tausaya ma kai na, gani na
ke kamar wani zai raba ni da ke. Don
Allah farida kada ki guje ni alhali sonki ya yi min mummunar kamu, bansan halin
da zan shiga ba idan na rasa ki.”
Maganganun sun shiga jikin
ta tausayin shi ya kama ta, sai dai ita kam ta san ba wanda take so banci shi
daya, to balle ya yi tunanin za su rabu, ba ta son irin maganganunnan su kan
tayar mata hankali. A hankali ta ke Magana cikin natsuwa, “ka daina sanya
wannan a ran ka, ka kwantar da hankalin ka insha’Allahu ba wanda zai raba mu face,
Ubangijin da ya hada mu, kawai mu ci gaba da du’a’i.” Ta na cikin maganar text ya
shigo wayar ta kamin ta duba wani text din ya sake shigowa, ba ta duba ba da
yake ta riga ta san lambar nan ce, da aka saba turo mata message, matsala daya
boye lambar da ake.
Fuskar ta ta nuna alamar
damuwa sai dai sam bata bari usman din ya fahimci wani abu ba, saboda bata son
Ya shiga damuwa. Da hakan kuma ya yi sallama da ita ya wuce.
Haka soyayyar ta su ta ci
gaba da gudana cikin tsafta da natsuwa,
a bangare guda kuma take kara samun yawan text
messages ga wayar ta,
wanda ba tada tabbacin mai text din. A dayan
bangaren kuma zuciyar ta na matukar damuwa da yadda Inna ke mata, tsanar da
Innar ke ma ta sai
karuwa take ta rasa dalilin tsanar.
Misalign sha biyu da rabi na
rana ta shirya cikin wani dakakken lace, kwalliyar ta yi matukar karbuwar ta,
sai wani kamshin turare take, mayafin ta kalar lace, din ne, takalmin ta yan flat ba masu tsini ba
sai yar hand bag din su mai kyau, ta fito fes da ita. Ta nufi sashen Mom din su
ta shaida mata Cewa za su fita, dama gidan Humaira Yayan na ta zai kai ta, Mom
din ta yi murmushi “ yar gidan daddy kinga yadda ki ka kara kyau kuwa?”
murmushi kawai ta yi ta fito, ta nufi wurin dalleliyar Jeep din da yayan na ta
ke jiran ta, ya bude mata gidan gaba ta shiga ta zauna, ya zagayo shima ya
shiga ya dan kalle ta, fuskar shi dauke da murmushi, “kanwa ta kinga yadda ki
ka yi kyau kuwa ? kwalliyar ta yi kyau”
ta dan yi murmushi “na gode da yabawa Yaya na”. A dai dai lokacin text ya shigo
wayar ta, yau dai ta dan daure ta karan ta.
Kalaman sun tsaya mata arai,
ta so tasan ainihin ko waye. Yayan na ta ya dan kalleta, hadi da tada motar ya
karanci damuwa tattare da ita, Sai dai ya ci gaba da tukin da yake ya damu
matuka baya son ya ga ta bata ran ta ko kadan, hakan da ta gani ya sa ta yi
saurin sake ran ta, sai dai zuciyar ta na cike da tunani daban daban. Sun dan
yi nisa da tafiya ya sake kallon ta, ya na yaba dabi’un ta du’a’in sa koda yau
she Allah ya zaba masa mata kamar kanwar sa.
Sun isa gidan Humaira ya yi
parking ta fito, dubu goma ya mika mata “karbi wannan kiba Humaira” ta nuna farin
cikin ta ta Karba hadi da godiya, sai zuwa azahar zai zo daukar ta.yayan na ta
yana matukar kula da ita, ya na son duk wani abun da take so, ya tsani damuwar
ta, yafi son ya gan ta cikin nishadi ko wane lokaci.sai dai abu daya sam baya son
kanwar tashi ta yi nisa da shi, sun shaku da juna sosai, wani lokaci har sukan
ba jama’a mamaki. Azahar na yi ya zo daukar ta Humaira ta rako ta hadi da
godiya, kawancen su son Allah ne aminci ne tsakanin su sun zama tamkar yan’
uwa.
*** *** ***
0 comments:
Post a Comment
Thank You for Your Comment