AZUMI DA FALALA
![]() |
https://i.ytimg.com/vi/PpxNRTdN3u0/maxresdefault.jpg |
Ramadan 2018 will begin in the evening of
Tuesday
,
15 May
Thursday
,
14 June
SHARAHBIL MUHAMMAD SANI
Copyright © Sharhamak, 2015
Hakkin Mallaka © Sharhamak, 2015
27th Sha’aban 1436AH
15th June, 2015CE
GODIYA
Auzu Billahis-Sami’ul Alim, Minash-Shaidanir Rajim.
Bismillahir Rahmanir Rahim.
Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin Sarki kuma aminci ya
tabbata a bisa zababben jakada Shugaban Annabawa Muhamamd Dan Abdullahi wanda
aka saukarma fiyayyen littafi (al-kur’ani) domin ya zama shiriya da kuma waraka
ga muminai.
Yarda da aminci su kara tabbata a bisa iyalan gidansa da
sahabbansa da kuma muminai har ya zuwa ranar karshe.
Bayan haka: Lalle Allah madaukaki Ya kimtsa mini kuma Ya
taimakeni akan na tarawa kaina day an uwana wani abu na daga fadakarwa kan
babban bakon da zai ziyarcemu a cikin yan kwanakin nan da basu wuce biyu ko uku
ba.
Hakika na cirato wasu bayanai daga maganganun wadansu malamai
tare da ayoyi da hadisai don ganin na cinasarar tsara wannan littafi. Ina yiwa
dukkan wadanda nayi amfani da wani abu nasu ta hanyar kafa hujja godiya da kuma
fatar Allah Ya biyasu Ya amfanar da su da ni da kuma Al’uma daga wannan littafi
amin.
Ina mika godiya tag a iyayena wadanda sune suka bani tarbiyya
har zuwa ga wannan hali da na tsinci kaina a cikinsa, ina rokon Allah Ya raya
mu tare da su Ya kuma kyautata rayuwarsu da mu Ya yiwa rayuwar albarka amin.
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
WASALLALLAHU ALA NABIYI AL-KARIM
WATAN RAMADAN
Allah madaukaki Yana cewa a cikin al-kur’ani: “Shi ne
wanda Ya sanya muku rana babban haske da wata mai haske, kuma Ya kaddara shi ga
Manziloli domin ku san kidayar shekaru da lissafi. Allah bai halitta wannan ba
face da gaskiya, Ya bayyana ayoyi daki-daki domin mutane wadanda suke sani”.
(Suratul Yunus).
Allah Ya halicci wata ne don mu san farko da karshen
watanni ta hanyar ganin shi. Wata yana kwana talatin ne (30) ba ya karawa akan
hakan, kamar yanda yake iya yin kwana ishirin da tara (29) baya kasawa ga hakan
don haka yana da muhimmancin gaske ga kowane musulmi yasan wadannan watannin
musulunci kamar yanda zan zano manasu. Wadannan sune ake cewa watannin
hijiriyya ko hilaliya ko kuma kamariya, kuma wadannan watannin su goma sha biyu
ne.
1.
Al-Muharram
2.
Safar
3.
Rabi’ul Auwal
4.
Rabi’ul Sani
5.
Jimadal Ula
6.
Jimadas Saniya
7.
Rajab
8.
Sha’aban
9.
RAMADAN
10.
Shawwal
11.
Zul-Ka’ada
12.
Zul-Hijja
Zamu ga cewa daga cikin wadannan jerin gwanon watannin
akwai wani wata mai suna RAMADAN wanda ya ke shine wata na tara kuma a
cikinsa ne aka wajabta yin azumi ma’ana a azumci watan gaba dayansa.
MENE NE AZUMI?
A yaren Larabci, shi ne kamewa daga barin ko mene ne,
kuma akan yi amfani da kalmar akan ko wane irin kamewa kamar yadda Allah
(S.W.T) ke bada labari akan Maryam (A.S) inda ta ke cewa “Lallai ni na yi
alwashi ga Allah mai rahama zan yi azumi”. (Suratul Maryam aya ta 26).
AZUMI A SHARI’ANCE
Shi ne kamewa daga abubuwa kamar Ci da Sha da kuma
Saduwa da iyali tun daga bullowar alfijir zuwa faduwar rana tare da niyyar
bautawa Allah Maigirma da daukaka.
Za a iya bashi wannan Ma’anar: Azumi shi ne niyar
azumtar dukkan kwanakin watan RAMADANA ta fuskar nisantar ababen da ke
bata azumin wadanda dukkansu suna komawa ne ga ababe uku ne kamar haka:
·
Barin cin duk wani nau’in abinci ko abin da ke cikin hukuncin shi, amma
ababen da basu da hukuncin abinci kamar aswaki ko kwalli ko saka turare ba su
bata shi.
·
Barin nau’ukan abin sha ko abin da ke da hukuncin abin sha kamar taba
amma abin da ba shi da hukuncin abin sha kamar wanka ko yawu ba ya cutar da
azumi
·
Nisantar tarawa da iyali ko duk wani abu wanda ke motsar da sha’awa,
amma sumbantar iyali ko rungumarsu ba ya bata azumi, duk da ya ke abin da ya fi
shi ne nisantar hakan.
Azumi yana daga cikin mafi girman da’a kuma Allah Yana
bada lada mara iyaka ga mai yin azumi, da azumi ake yin gafarar zunuban da suka
gabata kuma Allah Yana nisantar da fuskar mai yin azumi daga barin wuta, kuma
Yana cancantar da shigarshi aljanna. Muna rokon Allah Ya sanyamu daga cikin
wadanda zai yanta a cikin wannan wata na ramadana amin.
KASHE KASHEN AZUMI
Azumi Ya kasu kashi biyu kamar yadda zan zayyana mana
su kamar haka:
· Akwai azumi na wajibi (Dole ke
nan)
· Akwai azumi na nafila (Wanda ba
dole ba ko kuma a ce na neman lada yanda wadansu ke cewa)
Azumin wajibi ma’ana wanda yake dole kenan shi ma ya
kasu kashi uku.
· Akwai wanda yin shi dole ne a
wani lokaci ayyananne shi ne watan Ramadana
· Akwai wanda yake dole ne saboda
wani (illa) wato dalili wanda yake wajabta kamar kaffarar zihari ko na kisan
kai akan kuskure ko na rantsuwa da sauransu.
· Akwai wanda yake wajibi ne ta
hanyar mutum ya lizimtawa kansa yin azumi (kamar alwashi).
HUKUNCIN AZUMIN WATAN RAMADANA
Hukuncin yin azumin watan Ramadana wajibine ga kowane
Musulmi baligi mai hankali lafiyayye mazaunin gida kuma rukuni ne daga rukunnan
musulunci. Littafin Allah (Al-kur’ani) da sunna sun tabbatar da haka tare da
ijima’in malamai.
Allah maigirma da daukaka ya ce “Ya ku wadanda su kayi
imani! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka gabaceku
ko kwaji tsoron Allah”. (Suratul Bakara aya ta 183).
Manzon Allah (S.A.W) ya ce “An gina Musulunci akan
abubuwa guda biyar.
1. Shaidawa babu abin bautawa bisa
cancanta sai Allah kuma Annabi Muhammadu (S.A.W) Manzon Allah ne
2. Da tsayar da Sallah
3. Da bayar da Zakka
4. Da kuma aikin Hajji
5. Da Azumtar watan Ramadana
(Bukhari ya ruwaito shi Hadisi na 8 da Muslim Hadisi na 16 daga Abdullahi dan
Umar (Allah Ya yarda dashi)
Wani Balaraben kauye yazo wajen Manzon Allah (S.A.W)
kanshi a cukurkude ya ce “Ya Manzon Allah (S.A.W) bani labarin abin da Allah Ya
farlanta a kaina na azumi?” sai Manzon Allah (S.A.W) ya ce “Azumin watan
Ramadan sai dai kuma in ka so ka yi azumin nafila”. (Buhari Ya ruwaito shi
Hadisi na 50 da Muslim Hadisi na 9 daga Dalhatu dan Abdullahi (Allah Ya yarda
dashi).
Malaman Musulunci sun yi ijima’i akan cewa, azumi
rukuni ne daga cikin rukunnan Musulunci sanannu a cikin addini. Kuma Malamai
sun tabbatar da cewa ana iya kafirta wanda duk ya yi musun azumtar watan
Ramadan kuma azumin baya faduwa akan kowane balagagge mai hankali sai dai da
wani uzuri daga uzurorin shari’a wadda ta ke abin lura. (Al-Ifsah na Ibnu
Hubaira) Mujalladi na 1 shafi na 232 da (A-Mugny na Ibnu Kuddama) Mujalladi na
3 shafi na 285 da (Al-Majmu’u na Imamun Nawawi) Mujalladi na 6 shafi na 252.
SAHUR
Abincin da mai azumi yake ci kafin bullowar Al-Fijir
shi ake cewa (Sahur) kuma yana da kyau a jinkirta shi har kusan bullowar
Al-Fijir. Wannan kuwa abinci ne mai muhimmanci ga mai azumi don zai ba mai
azumi karfi.
Haka kuma yana kamata ga mai azumi a nan ma a lazimci
ladubban musulunci lokacin yin Sahur kamar haka: Ya ce “Bismillahi” Ya ci da
hannun dama kuma Ya ci gabanshi.
BUDA BAKI
Abin da mai azumi yake ci bayan faduwar rana shi ake
cewa (Buda Baki). Yana da kyau mai azumi ya gaggauta buda baki bayan faduwar
rana kada ya jinkirtar da yin buda baki har zuwa Sallar Isha’i kamar yanda masu
akidar Shi’a su ke yi.
ABUBUWAN DA AKA FI SO A BUDA BAKI DA SU
Misalin abubuwan da aka fi so a yi buda baki da su: Ya
halatta a bude baki da dukkan abincin da ya ke halal, duk da yake ana son a
bude baki da (DANYEN DABINO) idan bai samu ba sai a yi da (BUSASSHEN
DABINO) idan shima bai samu ba sai a bude baki da (RUWA KO WASU YAYAN
ITATUWA). Kuma ana son a lazimci ladubban cin abinci wadanda musulunci ya
tanada kamar yadda na fada a inda ya gabata wurin yin SAHUR.
FALALAR AZUMI DA FA’IDOJINSA
An karbo daga Abu Huraira (R.A) ya ce Manzon Allah
(S.A.W) ya ce “Duk wanda ya azumci watan Ramadana yana mai imani, yana mai
neman lada. To, an gafarta masa zunubansa wanda ya gabata. (Bukhari ya ruwaito
shi hadisi na 1900 da Muslim Hadisi na 760).
An karbo daga Abu Huraira (R.A) ya ce Manzon Allah
(S.A.W) ya ce “Idan watan Ramadana ya shigo ana bude kofofin sammai kuma ana
rufe kofofin wuta, ana kuma daure Shaidanu. (Bukhari ya ruwaito shi Hadisi na
1899 da Muslim Hadisi na 1079)
An karbo daga Sa’ad dan Sa’ad (R.A) ya ce “Manzon
Allah (S.A.W) ya ce “Lallai a cikin aljanna akwai kofofi guda biyu ana kiransu
da suna ARRAYYAN babu wanda zai shige su sai su (wato masu azumi). Za a
ce ina masu azumi? sai su mike sai a ce babu wanda zai shige ta wanda basu ba,
idan suka shiga sai a rufe kofar aljannar. Ba mai shiga wannan kofa ta ARRAYYAN
sai masu azumi”. (Bukhari ya ruwaito hadisin 1896 da Muslim Hadisi na 1152).
Daga Abu Huraira (R.A) ya ce Manzon Allah (S.A.W)
“Salloli biyar daga Juma’a zuwa Juma’a da kuma Ramadana zuwa Ramadana suna
kankare abin da ke tsakaninsu idan sun nisanci manyan zunubai. (Muslim ya
ruwaito shi Hadisi na 233).
An karbo daga Abu Huraira (R.A) ya ce “Lallai Manzon
Allah (S.A.W) ya ce”. “Allah Maigirma da daukaka ya ce”. “Dukkan ayyukan Dan
Adam nasa ne (ma’ana na mai aikin ne) amma banda azumi. Domin azumi nawa
(ma’ana azumi na Allah ne) kuma Ni ne zan yi sakayya ga mai yin azumi, domin
azumi garkuwa ne. duk ranar da mutum ke yin azumi baya zina baya daga murya
kuma baya yin wauta don idan wani ya zage shi ko ya neme shi da fada lallai ya
ce ni ina yin azumi (sau biyu) Manzon Allah (S.A.W) ya ce na rantse da wanda
raina yake a hannunsa warin bakin mai azumi yafi kamshi a wajen Allah ranar
kiyama daga kamshin turaren almiski, kuma mai azumi yana da farin ciki guda
biyu da zai yi farin ciki dasu lokacin da yake buda baki zai yi farin ciki da
lokacin da zai hadu da ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa”. (Bukhari ya
ruwaito shi Hadisi na 1904 da Muslim Hadisi na 1151).
Babban Malami Abu Amr Ibnu Abdul-Barri Al-Maliyy
(Allah Ya yi masa Rahama) ya ce “Fadin Manzon Allah (S.A.W) azumi nawa ne ni
zan yi sakayya da shi”. Ya ce “Wannan ya isa falala ga azumi akan sauran
ibadoji sai dai ya ce Malamai sun yi sabani akan abin da Allah (S.W.T) ya ke
nufi da azumi nawa ne, ni zan yi sakayya dashi tare da cewa kowane aiki nashi
ne (wato Allah S.W.T) kuma shi ne yake yin sakayya da shi, sun yi sabani mai
yawa (wato manyan malamai) na farko sun ce domin azumi riya ba ta shiga cikinsa
kamar yadda yake a cikin ayyuka. Imamul Kurdubi (Allah Ya yi masa Rahama) ya ce
“da yake ayyukan riya tana shiga cikinsu. To, amma azumi babu riya a cikinsu.
Domin shi aikin ana yin shi ne tsantsar shi ga Allah (S.W.T) shi ya sa Allah Ya
jinginashi zuwa gareShi (wato Shi ne ya ce azumi nawa ne, Ni ne zan yi sakayya
da shi). (Daga Asarabul Muhibbina Fi Ramadan Na Muhamamd Hussaini Yakub Shafi
na 18).
Al-Hafiz Ibnu
Rajab Al-Hambali (Allah Ya yi masa rahama) ya ce “Malamai sun yawaita maganganu
akan ma’anar fadin Manzon Allah (S.A.W) idan ya ce Allah (S.W.T) ya ce azumi
nawa ne zan yi sakayya da shi. Ya ce Malamai sun ce, lallai azumi shine raba
zuciya da sha’awoyinta na asali wanda Allah Ya dabi’anceta akan su karkata zuwa ga Allah (S.W.T) ya ce ba a
samun wannan a sauran ibadoji sai dai azumi kawai.
Na biyu suka ce “Lallai azumi sirri ne tsakanin bawa
da Allah (S.W.T) babu wata ibada da ked a wannan kuma niyya ce ta boye kuma ba
mai iya tsinkayar wannan sai Allah, kuma ya bar sha’awarsa wadda adabi’ance da
al’ada shi yasa babu riya a cikinsa ta inda mutum yana barin abin da zuciyarsa
ta ke kiransa zuwa gareshi na son sha’wa babu wanda ke iya tsinkayar wannan sai
Allah (Lada’iful Ma’arif Na Ibnu Rajab Al-Hambali Shafi na 209 – 212).
Idan mai azumi zai iya tafiyar da dukkan lokacin shi a
cikin ambaton Allah, abu ne mai kyau. Kamar karatun Al-kur’ani, sadaka, magana
mai kyau, kyawawan halaye da kuma rokon Allah har zuwa lokacin buda baki.
Ibn Abbas (R.A) yana cewa: “Manzon Allah (S.A.W) yafi
kowa kyauta kuma kyautar shi ta fi yawa a cikin watan Ramadan lokacin da
Mala’ika Jibril yake haduwa das hi kuma Jibril ya kasance yana haduwa da shi
cikin kowace rana ta Ramadan domin ya yi bitar Alkur’ani da Manzon Allah
(S.A.W) kuma Wallahi Manzon Allah (S.A.W) ya fi iska mai gudu kyauta.
Kuma bayan shan ruwa da sallar Isha’i yana da kyau a
yi sallar Asham tare da musulmi; domin a kasance daga cikin masu samu ladan
rana da daren watan Ramadan.
MUHIMMANCI DA WAJABCIN AZUMI
A watan Ramadana ne ayoyin Al-kur’ani na farko suka
sauka: Allah Ya na cewa “Watan Ramadana ne wanda aka saukar da Al-kur’ani a
cikinsa yana shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu daga shiriya da rarrabewa.
To, wanda ya halarta daga gareku a watan sai ya azumce shi”. (Suratul
Al-Bakrah).
Kamar yadda yake a bayyane Allah Ya umurci muminai da
su azumci wannan watan gaba dayan shi domin su godewa Allah game da ni’imar
wannan al’kur’anin da ke kunshe da shiriya da dadin kai ga talikai.
Idan namiji ya balaga ma’ana idan ya kai shekaru 15 ko
gashi ya fara tsirowa a gabansa ko ya ga maniyi a jikinsa to wajibi ne ya
azumci wannan wata.
Haka ne itama mace idan ta kai shekarun balaga ko ta
ga jinin al’ada ya zama wajibi akan tat a azumci wannan wata.
Kuma Manzon Allah (R.A) Ya kara mana bayani game da
shi wannan azumin inda ma har ya sanya shi daya daga cikin rukunnan musulunci
biyar. Don haka wajibi ne a kan baligi ya azumce shi gaba daya domin ya samu
falalar azumtar shi kuma ya kubuta daga ukubar Allah akan wanda ya sha azumin
wannan watan ba tare da uzuri ba.
Amma game da yaro wanda bai balaga ba, ba dole ba ne
ya yi azumi ba. Duk da yake ya kamata musulmi su horar da yayansu game da yin
azumi don su saba, don kada ya basu wahala idan sun girma.
Hakika duk lokacin da musulmi suka iske kansu a cikin
watan Ramadan, rayuwa takan sauya sukan koma ga Allah ta wajen gudanar da
ayyukan da’a. wadanda suke jin nauyin yin Sallah sukan motsa su rika yin ta a
kan lokaci cikin jama’a, masu sharholiya sukan rage ko su bari baga daya.
Saboda an daure shaidanu masu ingiza mutane ga sabon Allah.
Wannan duk albakarcin saukar da Al-kur’ani ne a cikin
watan Ramadana domin da azumin watan Ramadan din da sauran ayyukan da’a duk sun
biyo bayan saukar Al-kur’ani ne. saukarsa ce ta kawo duk wasu ayyukan alkhairi
da da’a dad an adam ke gudanarwa har zuwa yau ya alla a cikin watan Ramadana ne
ko a wanin watan ne na daban.
Kuma Al-kur’ani Maigirma ya bamu labarin dalilin
wajabta yin azumin a cikin fadar Allah madaukaki “Ya ku wadanda suka yi imani!
An wajabta azumi akanku kamar yadda aka wajabta shi akan wadanda suke a
gabaninku, tsammaninku za ku yi takawa. Kwanuka ne kidayayyu. To, wanda ya
kasance daga gareku majinyaci ko kuwa yana a halin tafiya sai ya biya adadi
daga kwanuka na daban. Kuma akan wadanda suke yinsa da wahala akwia fansa;
ciyar da matalauci sai dai wanda ya kara alkhairi, to, shi ne mafi alkhairi a gareshi.
Kuma ku yi azumin da wahalar ne mafi alkhairi a gareku idan kun kasance kuna
sani”. (Bakara 83 – 84)
Fa’idojin da zamu samu daga wadannan ayoyi biyu suna
da yawa, daga ciki akwai:
1.
Wanda ya samu kansa a cikin watan Ramadana yana cikin hankalinsa kuma
baligi. To, azumtarsa wajibi ne a kansa (Jami’ul Bayan Mujalladi na 3 Shafi na
454).
2.
Azumi yana daga cikin sabubban samu da ginuwar takawa a zukatan mutane
3.
Mai azumi yana tarbiyyantar da kansa ne kan tsoron Allah da kiyaye
dokokinSa (Allah). Ta barin abin da zuciyarsa ke so ko sha’wa alhali zai iya
boyewa ya aikata, amma sai ya ki saboda ya san Allah Yana ganinsa.
4.
Azumi yana takaitawa ko toshe magudanar shaidan. Domin Shaidan yana
gudana ne a jikin dan adam kamar yadda jini ke gudana. To, ta hanyar azumi sai
a raunana ikon gudanarsa sabo ya ragu.
5.
A galibi mai azumi ayyukansa na da’a na karuwa ayyukan da’a kuwa suna
daga cikin siffar takawa.
6.
Idan mawadaci ya dandani wahalar yunwa, hakan zai karfafa masa gwiwar
ya taimakawa talakawan da basu da, wannan ma siffa ce ta takawa.
7.
Allah Ya yi wa marasa lafiya da matafiya rangwame su ci abinci. To,
amma saboda irin maslahar da ke cikin azumi ga kowane musulmi, sai ya zamo Ya
umurce su da su rama abin da suka bari a wasu kwanuka na daban, lokacin da
ciwon ya warke ko aka dawo daga tafiya aka samu hutu. (Alfawa’id Mujalladi na 2
Shafi na 272).
8.
Azumi yana hana jindadi da sha’awoyin da zuciya ke ji, fiye da yadda
sauran ibadoji suke iya hanawa.
9.
Azumi sirri ne tsakanin bawa da ubangijinsa, babu mai riskar
hakikaninsa sai Shi (Allah), don haka ne Allah Ya ce naSa ne Shi zai saka a
kansa, sabanin sauran ibadoji na zahiri.
Sai aya ta gaba inda Allah Ya fayyace a wane wata za a
yi azumin cikin fadin Allah madaukaki “Watan Ramadana ne wanda aka saukar da
Al-kur’ani a cikinsa, yana shiryarwa ga mutane da hujjoji bayyanannu daga
shiriya da rarrabewa. To, wanda ya halarta daga gareku a watan sai ya azumce
shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko a kan tafiya, sai ya biya adadi daga
wasu kwanuka na daban, Allah Yana nufin sauki a gareku kuma ba Yana nufin
tsanani gareku ba kuma domin ku cika adadin kuma ku girmama Allah akan Ya
shiryar da ku, kuma tsammaninku zaku gode”. (Bakara aya ta 185)
Haka kuma akwai Hadisai da suke da nasaba da wannan
aya kamar:
Daga Abu Huraira (R.A) ya ce Manzon Allah (S.A.W) ya
ce “Wanda ya azumci Ramadan yana mai imani da neman lada an gafarta masa abin
da ya gabata na zunubinsa (Bukhari da Muslim)
Daga Abu Huraira (R.A) cewa Manzon Allah (S.A.W) ya ce
“Wanda ya yi tsayuwar Ramadan yana mai imani da neman lada an gafarta masa abin
da ya gabata na zunubinsa”. (Bukhari da Muslim)
Daga Jabir bin Abdullahi (R.A) Manzon Allah (S.A.W) ya
ce “Ku rika cin gajiyar saukin da Allah Ya yi muku (ma’ana matafiyi ya sha
azumi ya rama)” (Muslim)
Daga Muhajjinul Aslamiyyu ya ce Manzon Allah (S.A.W)
ya ce “Lallai mafi alkhairin addininku shi ne mafi saukinsa”. (Bukhairi)
Daga Anas bin Malik (R.A) ya ce “Manzon Allah (S.A.W)
ya ce “Ku saukaka, kada ku tsananta, ku zaunar kada ku kora”. (Bukhari)
A wannan aya fa’idojin da zamu samu sun hada da:
1. Falalar watan Ramadan saboda
saukar Al-kur’ani a cikinsa da kuma kebe shi da daren lailatul kadr. (Jami’ul
Bayan Mujalladi na 3 Shafi na 448)
2. Wajabcin azumtar Ramadan akan
daukacin mukallafai (Tafsirul Kur’anin Azim Mujalladi na 1 shafi na 206)
3. Sauki ga marasa lafiya da
matafiya kan su ci su sha a watan Ramadana da wajabcin rama abin da suka sha
(Fathul Kadir Mujalladi na 1 shafi na 281 – 282)
4. Saukin shari’ar Musulunci da
rashin tsananinta (Tafsirul Kur’anil Azim Mujalladi na 1 shafi na 206)
5. Shar’anta yin kabbarori a daren
Idi da Ranarsa domin godiya ga ni’imar Allah ta samun shiriya da Musulunci.
Shi kuma aya ta gaba na cewa: “Kuma idan bayiNa suka
tambaye ka daga gareNi, to lallai Ni makusanci ne. Ina karba kiran mai kira
idan ya kiraNi, saboda haka su nemi karbawaTa, kuma su yi imani daNi
tsammaninsu, su shiryu”. (Bakara aya ta 186)
Kasancewar mai azumi yana neman kusanci ga Allah ne da
rokonSa shiriya da sauran alkhairai sai Allah Ya nuna cewa Shi makusanci ne ga
masu kiranSa, amma da sharadin su nemi karbawarSa bayan sun yi imani da Shi.
Akwai Hadisai da dama da suke da alaka da abin da ayar take magana, daya daga
ciki shi ne Hadisin Abu Haraira (R.A) da ya ce “Manzon Allah (S.A.W) ya ce
“Lallai Allah Yana cewa: “Ina inda bawaNa yake zatoNa, kuma ina tare da shi
idan ya kiraNi.” (Muslim ya ruwaito shi) Fa’idojin wannan aya sun hada da:
1. Shar’antawa da mustahabbacin yin
addu’a. (Taisirul Karimur Rahman Shafi na 69)
2. Kusancin ubangiji ba ya lizimtar
cudanya, a’a Allah makusanci ne a cikin daukaka.
3. Makaruhancin daga sauti a lokacin
ibada, face wadannan ibadu kamar haka:
i.
Talbiyya
ii.
Kiran Sallah
iii.
Da ikama (Aisarut Tafsir Mujalladi na 1 shafi na 165)
4. Wajabcin amsawa da mika wuya ga
umurnin Allah. (Jami’u Ahkamil Kur’an Mujalladi na 2 shafi na 313)
5. Amsa kira da bin umurnin Allah
yana gadar da shiriya da dacewa. (Taisirul Karimir Rahman shafi na 69).
Aya ta gaba kuma sai ta ce “An halatta a gareku a
daren azumi yin tarayya zuwa ga matanku, su tufa ne a gareku, kuma tufa ne a
garesu, Allah Ya sani lallai ku kun kasance kuna yaudarar kanku. Saboda haka Ya
karbi tubarku kuma Ya yafe muku. To, yanzu ku rungume su, kuma ku nemi abin da
Allah Ya rubuta muku. Kuma ku ci ku sha har silili far ya bayyana a gareku daga
silili baki daga alfijir, sannan ku cika azumi zuwa ga dare. Kuma kada ku
rungume su alhali kuna masu I’itikafi a cikin masallatai. Wadannan iyakokin
Allah ne: don haka kada ku kusance su, kamar haka ne Allah Ya ke bayyana
ayoyinSa ga mutane tsammaninsu za su yi takawa”. (Bakara 187)
Allah mafi girma! Dubi yadda ayar farko an rufe ta da
takawa, haka kuma dubi yadda aka rufe aya ta karshe da batun takawa bayan Ya yi
magana kan abubuwan da aka halatta ga mai azumi da dare. Wannan yana nuna
kashin bayan yin azumi shi ne a samu takawa.
Fa’idojin da wannan aya take koyarwa sun hada da:
1. Halaccin ci da sha da tarayya a
dararen azumi bayan ya kasance haramtacce idan aka yi barci a baya. (Jami’ul
Bayan Mujalladi na 3 shafi na 464).
2. Lokacin azumi ana faraway ne daga
ketowar alfijir zuwa faduwar rana. (Aljami’u Li’ahkamil Kur’an Mujalladi na 2
shafi na 319).
3. Ana son yin amfani da kinaya
maimakon bayyanawa baro-baro a abin da akwai kunya a cikinsa. (Aljami’u
Li’ahkamil Kur’an Mujalladi na 2 shafi na 315)
4. Shar’anta I’itikafi a cikin watan
Ramadana da yankewa daga mutane domin yin ibada. Kuma mai I’itikafi bai halatta
a gareshi ya ji dadi da matarsa har sai
lokacin da I’itikafinsa ya kare. (Tafsirul Kur’anil Azim Mujalladi na 1 shafi
na 213).
5. Haramcin keta hurumin shari’a da
ke tare haddodinta. (Tafsirul Kur’anil Azim Mujalladi na 1 shafi na 213)
Bayyana makasudin saukar da shari’o’I da sanya haddodi
wato takawa ga Allah madaukaki. (Ruhul Ma’ani Mujalladi na 2 shafi na 69)
ABUBUWAN KI GA MAI AZUMI
Idan musulmi yana cikin halin azumi ya kamata ya
nisanci dukkan abin da ya kasance haram ko makaruhi; ya nisanci fasikanci da
maganar alfasha da daga murya a cikin magana da hayaniya ko da wani ya neme shi
da fada ya ce da shi “Ni mai azumi ne”.
Kamar yanda ya zo a cikin Sahih Bukhari Manzon Allah
(S.A.W) yana cewa “Wnda bai bar magana zur ko aiki da shi ba, Allah ba ya
bukatar wannan mutum ya bar abincinsa da abin shansa”.
Kuma Manzon Allah (S.A.W) ya ce “Azumi garkuwa ne don
haka mai azumi ya nisanci fasikanci da jahilci, idan wani ya ya keshi ko ya
zage shi ya ce da shi; “Ni mai azumi ne”. (Bukhairi ya ruwaito shi)
UZURI LOKACIN AZUMI
Idan mai azumi ya ci abinci da mantuwa ko kuma ya sha
wani abin sha, to ya cigaba da azuminsa kuma ba zai ranka ba bayan Ramadana.
Kuma haka ne ma idan mutum ya kasance bai sani ba sai
ya ci ko ya sha, sai da ya kammala azuminsa idan ya samu sani; saboda shi ma
jahilci uzuri ne karbabbe a cikin musulunci.
Wannan kuwa duk daya ne; da wanda bai san hukuncin ba,
ko kuma ya jahilci shigar lokaci ko fitar shi kuma shi ma ba zai ranka wannan
azumin ba a bayan Ramadana.
Kuma haka ne idan aka tilasta mutum ya ci ko ya sha
saboda tilastawa uzuri ce karbabbe.
Haka ma mai barci idan ya yi mafarki kuma maniyi ya
zubar mishi sai ya yi wanka ya cigaba da azuminsa.
Haka ne idan mutum ya kasance a cikin halin tafiya
(balaguro) yana da damar ajiye azumi bayan watan ramadana sai ya ranka wannan
yinin idan kuwa tafiyarshi a kwana biyu ne kuma ya ajiye azumi na tsawon kwana
biyu sai ya ranka wandannan kwanaki biyu; a takaice zai ranka iya kwanakin da
ya sha.
Idan kuma matafiyi ya ga yana iya yin azumi to ba dole
ba ne ba, sai ya sha ruwa domin shan ruwa sauki ne da Allah Ya bashi, yana da
damar yin azumi: ya dubi abin da ya fi sauki gare shi sai ya aikata.
Kuma dukkan abin da ya yi kama da rashin lafiya ana
bashi hukuncin rashin lafiya misali; mutum ya yi kaho ya fitar da bataccen
jini, ko kuma ya bada jini lafiyayye sai ya samu raunin jiki kamar mara lafiya.
Haka ma mace idan taga jinin al’ada wajibi ne akanta
ta bar azumi sai ta ranka kwanakin da ta sha bayan watan Ramadana.
Ita ma mai biki ya haramta a kanta ta yi azumi kuma
bayan watan Ramadana ita ma za ta ranka ranakun da ta sha.
Amma mace mai ciki ko mai goyo idan azumin ya kasance
zai cutar da ita ko zai cutar da dan ta sai ta ajiye azumin sa’annan bayan
Ramadana sai ta ranka iya kwanakin da bata azumta ba, kuma yana da kyau ta
ciyar da miskini guda dukkan wuni bayan ta ranka azumin.
Mutunen da kuma ba shi da karfin yin azumi kuma
likitoci suka tabbatar mishi cewa ba zai iya yin azumi ba, to wajibi ne akan
shi ya yi sadaka; wannan sadakar ita ce: ciyarda miskini guda ko wace rana da
bai azumta ba; kenan zai ciyar da kwatankwacin abincin da zai ishi miskini
talatin ya ciyar da miskini talatin abincin da zai ishe su.
RANAR IDI
Idan musulmi suka gama azumtar watan Ramadana gaba
daya, ranar farko ta watan Shauwal Idi ne na musulmi; shi ne kuma ake kira idin
samun baki ko buda baki bayan watan azumi. A cikin wannan rana musulmi suna
nuna farin cikinsu saboda Allah Ya basu damar cika ibadar azumtar watan
Ramadana.
Kuma suna nuna farin cikinsu ne ta fuskoki masu awa
daga cikinsu akwai:
·
Nuna farin ciki ta fuskar yawan godiya ga Allah madaukaki.
·
Yawaita kabarbari da girmama Allah; don haka tun daga daren Idin har
zuwa safiya suna yawaita cewa (Allahu Akbar, Walillahil Hamd)
·
Suna yin sadaka ko wane magidanci zai fitar da kwatankwacin kilo uku na
alkama ko shinkafa ko abincin mutanen wannan garin ga duk wanda ciyar dashi ya
rataya a wuyanshi.
·
Suna nuna farin cikinsu ta hanyar halartar sallar Idi bayan bullowar
rana da dan lokaci kadan; inda suke sallar raka’a biyu a cikin jama’a, suna
masu sanya tufafi masu kyau mafifita. Wannan duka yana nuna mana cewa idin
musulmi babu nuna jiji da kai ko shan giya ko abin da yayi kama da haka a cikin
shi, sabanin yanda yake wajen wadanda ba musulmi ba. Idi ne na biyayya ga Allah
da yin sadaka da sadar da zumunta da rahama da gafartawa juna tare da yin
sulhu… Suna masu jiran babban Idi yayin da za su kasance a cikin al’janna suna
matasa, kuma babu mutuwa ko tsufa ko ciwo ko tabewa. Wannan kuma shine babban
rabo.
Wannan kuma shi yasa musulmi ya ke rayuwa a nan duniya
cikin kwancin hankali da yarda da halin da yake ciki duk yanda ya kasance a
cikin musiba domin ya san abin da ke wajen Allah gobe kiyama. Allah Yana cewa “Kuma
abin da aka basu daga kome, to, jin dadin rayuwar duniya ne da kawarta. Kuma
abin da ke wurin Allah, shi ne mafi alkahiri kuma mafi wanzuwa. Shin ba ku
hankalta?”. (Suratul Al-Qasas).
Daga karshe ina rokon Allah daya datar damu
alkhairinSa tun a nan duniya Ya kuma taimake mu Ya sanya mu a cikin RahamarSa a
Lahira Ya sanya mu aljannarSa madaukakiya amin.
Daga mai kaunar Rahamar UbangijinSa mai yawan kyauta.
Sharahbil Muhammad Sani
0 comments:
Post a Comment
Thank You for Your Comment